An roƙi Joe Biden da yasa baki Najeriya ta saki jami’in Binance

0 164

Wakilan Majalisar Dokokin Amurka 16 sun roƙi Shugaba Joe Biden da ya shiga tsakani don ganin an saki babban jami’in kamfanin hada-hadar kuɗin intanet, Binance, Tigran Gambaryan, wanda ake tsare da shi a Najeriya tun a watan Fabarairu.

Gwamnatin Najeriya ta kama Gambaryan inda yake fuskantar tuhumar ƙin biyan haraji da kuma yadda kamfanin ke taimaka wa masu hada-hada wajen kauce wa haraji.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa ƴan majalisar sun ce a matsayin Gambaryan na ɗan Amurka, bai dace gwamnatin wata ƙasa ta tsare shi ta hanyar da ba ta dace ba, har ma a riƙa gallaza masa.

Ƴan majalisar sun kuma bayyana damuwarsu kan lafiyarsa.

‘Yan majalisar sun ce suna buƙatar taimakon gwamnatin Biden domin mayar da Gambaryan ƙasarsa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: