Asusun yan fansho ya kammala biyan hakkokin iyalan ma’aikata 86 da suka mutu a bakin aiki
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2021/08/money-5.jpg?resize=612%2C408&ssl=1)
Asusun yan fansho na Gwamnatin jihar jigawa dana kananan hakumomin jiha yace ya kammala biyan dukkan hakkokin iyalan ma’aikata 86 da suka mutu a bakin aiki na sama da naira miliyan 292.
Babban sakataren asusun Alhaji Kamilu Aliyu Musa ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.
Yayi bayanin cewa, ma’aikata 577 da suka kammala shekaru 35 na aiki sun samu hakkokin su da suka tasamma sama da naira biliyan 1 da rabi na kudaden giratuti.
Alhaji Kamilu Aliyu Musa ka kuma kara da cewa iyalan yan fansho 38 da suka rasu kafin cika shekaru 5 da yin ritaya suma an biya su naira miliyan 33 da dubu 538 ta hannun magadansu. Kazalika Hakumar ta biya sama da naira biliyan 1 da miliyan 800 a matsayin hakkokin tsaffin ma’aikata sama da 700 da suka yi ritaya daga matakan aikin gwamnatin jiha da kananan hakumomi.