Gwamnan jihar Yobe ya jinjinawa sojojin Najeriya kan yadda suka fatattaki mayakan Boko Haram

0 126

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya jinjinawa sojojin kasar kan yadda suka fatattaki mayakan Boko Haram, bayan da suka gudanar da manyan ayyuka a ma’aunin Tumbuktu na dajin Sambisa.

Buni ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin sabon kwamandan runduna ta 2, ta Operation Hadin Kai, Birgediya Janar Marcel Ejike, a ofishinsa da ke Damaturu, babban birnin jihar.

Ya kuma yi alkawarin tallafawa gwamnati ga dukkan hukumomin tsaro a jihar Yobe.x  q

Gwamnan ya yabawa sojojin da suka samu karin nasarori ta hanyar shiga na dajin Sambisa domin tabbatar da cewa an samu cikakken zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

Kwamandan ya mika wa gwamnan takardar karramawa bisa goyon bayan da ‘yan kasar ke baiwa sojoji a jihar.

Leave a Reply

%d bloggers like this: