Gwamnan Kaduna Ya Bayar Da Kwangilar Wasu Manyan Aiyuka

0 101

Gwamnan jihar Kaduna Nasir El’Rufa’I ya rattaba hannu kan wasu kwaskwarima manyan ayyuka da suka hada da tutuna a fadin jihar wanda wani kamfani kasar China zai gudanar da aikin.

Yayin kaddamar da aikin gwamnan ya ce wannan aiki shi ne mafi inganci aikin kwaskwarimar aiki da za’ayi a tarihin jihar Kaduna.

Ya ce ayyukan gyare gyaren da za’a gudanar zai sanya kyakkywar makobtaka tsakanin al’ummomin jihar da sauran makobtan jihar.

Kazalika gwmna Nasir El-Rufa’I ya bukaci al’ummar jihar da su bada goyon baya domin samun nasarar aikin, wanda zai shafi buda tituna da kuma cire wadansu gina ginan al’umma.

Leave a Reply

%d bloggers like this: