Gwamnan jihar Kaduna Nasir El’Rufa’I ya rattaba hannu kan wasu kwaskwarima manyan ayyuka da suka hada da tutuna a fadin jihar wanda wani kamfani kasar China zai gudanar da aikin.
Yayin kaddamar da aikin gwamnan ya ce wannan aiki shi ne mafi inganci aikin kwaskwarimar aiki da za’ayi a tarihin jihar Kaduna.
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2019/06/IMG_20190628_131424.jpg?resize=850%2C646&ssl=1)
Ya ce ayyukan gyare gyaren da za’a gudanar zai sanya kyakkywar makobtaka tsakanin al’ummomin jihar da sauran makobtan jihar.
Kazalika gwmna Nasir El-Rufa’I ya bukaci al’ummar jihar da su bada goyon baya domin samun nasarar aikin, wanda zai shafi buda tituna da kuma cire wadansu gina ginan al’umma.