Gwamnati ta lalata hauren giwa mai ƙimar tsabar kuɗi har dala miliyan 11

0 173

Gwamnatin tarayya ta lalata tarin hauren giwa mai ƙimar tsabar kuɗi har dala miliyan 11 da ta ƙwace daga hannun masu fasa-ƙwauri.

An dai yi fasaƙwaurin hauren ne daga ƙasashen Afirka da dama.

Ministan Muhalli na kasa, Iziaq Adekunle Salako wanda ya shaida hakan yayin wani taro a Abuja, ya ce ya ɗauki matakin lalata tarun hauren giwar ne domin aike saƙon da ke nuna rashin amincewarsu ga irin wannan aiki.

Masana sun ce ana kashe dubban ɗaruruwan giwaye a kowace shekara domin yin safarar haurensu, duk da haramcin cinikayyarsu da duniya ta yi shekaru da suka gabata. Masu kare dabbobi sun ce Najeriya ta zamo a gaba-gaba wajen safarar sassan dabbobi.

Leave a Reply

%d bloggers like this: