Indiya ta mika ragamar jagorancin kungiyar G20 ga shugabancin kasa Brazil

0 226

Indiya ta mika ragamar jagorancin kungiyar G20 ga shugabancin kasa Brazil, a wani kebabben bikin shekara-shekara da kungiyar ta gudanar a birnin Delhi a karshen makon daya gabata.

Fira Ministan Narendra Modi ya kammala mika shugabancin ga shugaba Luiz Inacio Lula da Silva na Brazil.

India ta kasance ta jagorancin kungiyar tun 1 ga watan desemba lokacin da ta karba da Indonesia inda tacigaba da rike matsayin har ranar 30 ga watan Nuwamba. Yayin taron na kwanaki 2, kungiyar ta cimma matsaya kan lamura da dama da suka hada da samar da abinci da makamashi, sauyin yanayi da kuma karuwar lamuri.

Leave a Reply

%d bloggers like this: