

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
An bayyana Jami’ar gwamnatin tarayya dake Dutse babban birnin jihar Jigawa, a matsayin jami’ar da ta fi fice a cikin jami’oi 12 da gwamnatin tarayya ta gina a 2011.
Shugaban hukumar dake kula da jamioi ta kasa (NUC) Farfesa Abubakar Adamu Rasheed ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Abuja.
Ya ce jami’ar ta FUD ta kaddamar da bikin sababbin dalibai har sau 8 daga cikin wadanda aka kirkire su tare yayin da su kuma ke kokarin gudanarda bikin a karon farko.

Rasheed ya ce an samu cigaba sosai a jami’ar sakamakon fadi tashin da shugabannin jami’ar ke yi karkashin jagorancin Farfesa JD Amin, da kuma Farfesa Fatima Batul-Muktar.
Kazalika ya yabawa al’ummar jihar Jigawa da kuma gwamnatin jihar bisa taimakon jami’ar wajen gudanar da ayyukanta.