

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Kudirin kafa bankin cigaban ma’adanan kasa ya tsallake karatu na biyu a majalisar dattawa.
Kudirin wanda Yakubu Oseni na jam’iyyar APC daga Kogi ta tsakiya ya dauki nauyinsa, na neman kara bunkasa zamantakewa da tattalin arziki mai dorewa.
Haka kuma ana kokarin inganta fannin ma’adanai da ingancin rayuwar al’umma ta hanyar samar da jarin kudade a fannin.
‘Yan majalisar dai sun kayyade kudi naira biliyan 500 domin kafa bankin.
An karanto kudirin dokar a karo na biyu bayan Yakubu Oseni ya jagoranci muhawara akai a jiya.
Kudirin, in ji shi, an samar da shi ne da nufin samar da kudaden da ake bukata na bangaren ma’adanan kasa a kasarnan.
Bayan kammala karatu na biyu, an mika kudirin ga kwamitin majalisar dattawa mai kula da ma’adanai domin bayar da rahoto nan da makonni hudu.