Mai ɗaukar hoton gidan Talabijin ɗin Aljazeera ya rasu sakamakon hare-haren Isra’ila a Gaza

0 217

Gidan talabijin din na Aljazeera ya bayyana cewa harin jirgi marar matuƙi ne da Isra’ila ta kai a wata makaranta dake Khan Yunis ya kashe Samer Abu Daqqa.

Ma’aikacin na Aljazeera ya ta zubar da jini har ya rasu sakamakon rashin isar masu ceto a makarantar. Aljazeera ta zargi sojojin Isra’ila da hana shigar motar marasa lafiya makarantar da lamarin ya faru da gangan, sai dai sojojin Isra’ilar ba su ce komai kan hakan ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: