Mataimakin gwamnan jihar Jigawa ya bukaci masu shirya fina-finan Hausa da su kiyaye ka’idoji da aladu na mutanen jihar jigawa

0 71

Mataimakin gwamnan jihar Jigawa Mallam Umar Namadi ya bukaci masu shirya fina finan Hausa da su kiyaye da kaidoji da dokoki da aladu da kuma addinin mutanen jihar jigawa

Ya yi wannan kiran ne a lokacin da mai shirya wasan hausa na Kwana Casa’in a tashar talabijin ta Arewa 24 ya ziyarci ofishinsa

Mallam Umar Namadi yace gwamnatin jiha a shirye take wajen tallafawa duk wata kungiya da take da Muradin dabbaka aladu da Muradin alummar jihar nan

Ya kuma yi gargadin cewar gwamnati ba zata laminci duk wani abu da ka iya zubar da kima da kuma mutuncin jihar da alummar jihar nan baki daya

Tun farko a jawabinsa babban jamiin shirya wasan Hausa na Kwana Casa’in, Mr Evans Ejiogu yace sun ziyarci ofishin mataimakin gwamna ne domin godewa gwamnati bisa hadin kai da goyan bayan da take basu wajen shirya Shirin Kwana Casa’in a jihar jigawa

Inda ya bada tabbacin cigaba da kiyayewa da dokoki da kuma kaidojin da aka shimfida musu

Leave a Reply

%d bloggers like this: