Gwamnatin kasar Algeria za ta fara biyan tallafin rashin aikin yi sama da 41,000 ga matasa masu tasowa

0 76

Gwamnatin kasar Algeria za ta fara gabatar da tallafin rashin aikin yi ga matasa masu tasowa a daidai lokacin da kasar ke fama da matsalar rashin ayyukan yi.

Shugaban kasar Abdelmadjid Tebboune ya shaida wa manema labarai cewa za a fara biyan matasa marasa aikinyi daga shekaru 19 zuwa 40 tindaga watan Maris din wannan shekarar

Wadanda suka cancanta za su na samun Dalar amurka $ 100 kimanin naira dubu 41,700 a kowanne  wata, da kuma wasu fa’idodin kiwon lafiya, har sai sun sami aiki.

Da yake bayyana hakan, Mista Tebboune ya ce Algeria ce kasa ta farko a wajen Turai da ta bullo da irin wannan kudirin mai mahimmancin gaske.

Ya kara da cewa yanzu haka akwai marasa aikin yi sama da 600,000 a Aljeriya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: