Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayar da dama ga ma’aikatar sufurin jiragen sama ta tarayya da ta hana dukkan hadiman masu rike da mukaman siyasa da sauran manyan mutane daga shiga wajen zaman jira a filayen jiragen sama.
A cewar ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika, an haramtawa dukkan hadiman manyan mutane zuwa filayen jiragen sama, matukar ba iyayen gidansu ne za suyi tafiya ba.
Hadi Sirika ya kuma bayyana cewa dukkan fasinjan da yaki sanya abin rufe baki da hanci, baza a kyale shi ya hau jirgin sama ba, bayan an dawo da jigilar jiragen saman a gobe, farawa da filayen jiragen saman Abuja da Lagos.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
Ministan ya sanar da haka a taron manema labarai na kwamitin karta kwana na shugaban kasa akan cutar corona a Abuja. A cewarsa, ba a amince da zuwa da makamai filayen jiragen sama ba.
Akan ko za ake bayar da tazara a cikin jiragen sama, Hadi Sirika yayi bayanin cewa babu wata barazana a dakunan jiragen sama, inda ya bayyana iskar cikin jiragen sama a matsayin tsaftatacciya wacce aka tace.