Shugaba Buhari yana kira ga ƴan Najeriya da su sake farfado da fata nagari da nuna soyayya ga juna koda ba addinin su daya ba

0 158

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su sake farfado da fata nagari a kasarnan, inda ya bukace su da su yi amfani da lokacin Kirsimeti wajen nuna soyayya ga junan su.

A sakonsa na Kirsimeti a yau, Buhari ya ce ya kamata ‘yan Najeriya su yi amfani da lokacin bukukuwan don karfafa wa juna gwiwa, ta yadda makircin miyagu ba zai samu gindin zama ba.

Shugaba Buhari ya ce gwamnatinsa ta tsaya tsayin daka wajen ganin an daukaka darajar rayuwar talakawan Najeriya.

Akan yaki da rashin tsaro, shugaba Buhari ya ba da tabbacin cewa da sabbin alkawurran da hukumomin tsaro suka dauka, nan ba da jimawa ba ‘yan Najeriya za su samu cigaba.

A cewar sa, gwamnatinsa na ci gaba da tallafawa jami’an tsaro wajen gudanar da ayyukansu.

Ya kuma yi amfani da sakon wajen yin kira ga dukkan ‘yan Najeriya da su yi allurar rigakafin cutar corona.

Leave a Reply

%d bloggers like this: