

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan fashin daji ne sun kai farmaki kauyen Kurawa da ke karamar hukumar Sabon Birni a jihar Sokoto, inda suka kashe mutane uku.
Harin dai ya faru ne sa’o’i kadan bayan gwamnan jihar Aminu Waziri Tambuwal ya bar yankin.
Tambuwal ya ziyarci Sabon Birni ne domin kai ziyarar jaje ga iyalan matafiya da ‘yan bindiga suka kone kurmus a hanyar Sabon birni zuwa Isa ranar Litinin.
Gwamnan ya sanar da bayar da gudunmuwar kudi naira dubu 250 ga iyalan kowane mamaci.
An rawaito cewa ‘yan bindigar sun mamaye kauyen ne da misalin karfe 8 na daren jiya, inda suka rika harbe-harbe.
An kasa samun kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Sakkwato, ASP Sanusi Abubakar, domin jin ta bakinsa.