

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Allah yayiwa Tsohon Shugaban Kasar Masar, Mohammed Morsi Rasuwa bayan faduwa da yayi a gaban kotu a Yau Litinin.
Kafar yada labaran Talabijin ta kasar Masar ta bayyana cewa Tsohon Shugaban kasar ya rasu ne yayin da ake zaman kotu don sauraron kararsa da ake yi.
Rahotanni sun ce ya suma ne a yayin zaman kotun inda ake tuhumarsa da laifukan cin amanar kasa, jim kadan bayan sumar tasa sai ya cika. Ya bar duniya yana da shekara 67.
Morsi Dai Sojoji ne suka Hambarar dashi bayan ya lashe zaben Kasar ta Masar a Shekarar Dubu Biyu da Sha Ukku a wani Yanayin Juyin Juya Hali.