

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
A halin da ake ciki, shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskyy a cikin wani faifan bidiyo ya ce an kashe fararen hula da sojoji 137 a kasar a ranar farko ta mamayar Rasha tare da jikkata 316.
Ya bayyana wadanda abin ya shafa a matsayin jarumai.
Ya ce sojojin Rasha suna kashe mutane tare da mayar da garuruwan zaman lafiya zuwa sansanin soji, inda ya kara da cewa wannan zalunci ne kuma ba za a yafe ba.
Ana sa ran adadin zai karu bayan hare-haren baya-bayan nan, ciki har da wadanda aka kaddamar a birnin Kyiv da safiyar yau.
Ya kuma bayyana takaicinsa kan sakamakon tattaunawar da ya ce ya yi da shugabannin kasashe mambobin kungiyar tsaro ta NATO.
A cewar kwamishinan hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, Filippo Grandi, sama da ‘yan Ukraine dubu 100 ne suka kauracewa gidajensu domin neman tsira, sannan dubbai ne suka tsallaka zuwa kasashen Moldova, Romania da sauran kasashe makwabta.