

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Kwamitin koli kan harkokin addinin musulunci ya bukaci musulmai a kasarnan da su fara duban sabon watan musulunci na Shawwal daga ranar Juma’a, 22 ga watan Mayu.
Kwamitin ya fadi haka cikin wata sanarwa da mataimakin Sakatare Janar na kwamitin, Salisu Shehu, ya fitar jiya Litinin a Abuja.
Salisu Shehu ya kuma taya musulmai murnar gudanar da azumin watan Ramadan na bana, inda yayi addu’ar Allah (SWT) ya bawa dukkan musulmai damar ganin wani watan na Ramadan cikin koshin lafiya.
Daga nan sai yayi kira ga musulmai a fadin kasarnan da su saurari sanarwar shugaba na kasa na kwamitin koli kan harkokin addinin musulunci, dangane da karshen azumin watan Ramadan na bana.