Ba na tsoron mutuwa tunda na haura shekaru 60 a duniya – Remi Tinubu

0 103

Uwargidan shugaban kasa, Remi Tinubu, ta ce ba ta tsoron mutuwa saboda tana da shekaru sama da 60 a yanzu.

Ta bayyana hakan ne a jiya Talata yayin da take mayar da martani ga kalaman Gwamna Bala Mohammed game da barazanar da aka yi mata a baya-bayan nan.

Tun da farko Bala Mohammed ya yi Allah-wadai da barazanar da aka yiwa uwargidan shugaban kasa a kwanakin baya inda ya bayyana hakan a matsayin abin kunya ga kasa. Sai dai a nasa jawabin mai martaba Sarkin Bauchi, Alhaji Biliyamin, ya yi watsi da rade-radin da ake yi na cewa Bauchi ba ta daga cikin jihohin masu zaman lafiya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: