

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Babban bankin kasa (CBN) yace ya raba sama da naira tiriliyan 1 da miliyan dubu 300 domin tallafawa samar da wutar lantarki ga ‘yan Najeriya cikin shekaru 5 da suka gabata.
Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, shine ya sanar da haka a jiya wajen taron manema labarai biyo bayan wata ganawa da kwamitin masu harkar bankuna a Abuja.
Emefiele yace bankin ya bada naira miliyan dubu 11 da miliyan 110 ga masu ruwa da tsaki a bangaren wutar lantarki a ka0 rkashin shirin kasuwancin wutar lantarki.
Sai dai, Emefiele ya sha alwashin jajircewar bankin wajen cigaba da tallafawa kamfanonin rarraba wutar lantarki domin samar da tsayayyar wutar lantarki ga ‘yan Najeriya.
Emefiele ya kuma ce bankin na CBN zai fara bayar da tallafi ga kamfanin mai na kasa NNPC da nufin tabbatar da cewa ya shigo da albarkatun man da zai kawo karshen karancinsu a kasarnan.