

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya ce shugabannin kasashen kungiyar ECOWAS sun sake jaddada matsayarsu na cewa kwata-kwata babu wani uzuri na sauya gwamnati ta hanyar juyin mulki.
Ya bayyana hakan ne a jiya bayan halartar babban taron kungiyar ECOWAS da aka gudanar a Accra, babban birnin kasar Ghana, kuma tattaunawar da aka yi a taron ta shafi harkokin siyasa a kasashen Burkina Faso, Mali da Guinea.
Mataimakin shugaban kasar ya ce a ra’ayin kungiyar ECOWAS, hanya daya tilo ta sauya gwamnati a yankin da aka amince da ita, ita ce ta hanyar demokradiyya.
Farfesa Osinbajo wanda ya wakilci shugaban kasa Muhammadu Buhari a wajen taron, ya amsa tambayoyi daga manema labarai kan sakamakon taron.
A wata sanarwa da kakakinsa Laolu Akande ya fitar, ya ce mataimakin shugaban kasar ya dawo Abuja da yammacin jiya daga birnin Accra.