Gwamnati tarayya ta sanar da cewa a yanzu haka, an bude tashoshin jiragen sama 14 da ke fadin kasar nan, domin sufurin cikin gida na yan kasuwa.
Sanarwar hakan ta fito ta hannun Ministan Sufirin Jiragen Sama Hadi Sirika wanda ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa, tashshin jiragen sun dawo bakin aiki.
Sirika ya zayyano tashoshin jiragen saman, da suka hadar da na Murtala Muhammad dake Lagas, da filin jirgin Nnamdi Azikiwe dake Abuja, da kuma na Malam Aminu Kano dake jihar Kano, sannan filin sauka da tashin jirage na kasa da kasa na Portharcourt dake Omagwa.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Sauran sun hadar da filin jirgin Sam Mbakwe na Owerri, da kuma na Maiduri, sai filin jirgin Victor Atta dake Uyo, da kuma na Kaduna da Yola.
Sirika ya kara da cewa a kwai tashar Ekpo na Calaba da kuma Sultan Abubakar dake Sokoto, sannan filayen jirgin sama na Birnin Kebbi da Yakubu Gowon da ke Jos, sannan tashar jirgin Benin dake Jihar Edo.
Ministan ya ce bayan kammala dukkan shirye-shirye, an amince da tashoshin jiragen guda 14 su dawo bakin aiki.