Gwamnati tarayya ta sanar da cewa a yanzu haka, an bude tashoshin jiragen sama 14 da ke fadin kasar nan, domin sufurin cikin gida na yan kasuwa.
Sanarwar hakan ta fito ta hannun Ministan Sufirin Jiragen Sama Hadi Sirika wanda ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa, tashshin jiragen sun dawo bakin aiki.
Sirika ya zayyano tashoshin jiragen saman, da suka hadar da na Murtala Muhammad dake Lagas, da filin jirgin Nnamdi Azikiwe dake Abuja, da kuma na Malam Aminu Kano dake jihar Kano, sannan filin sauka da tashin jirage na kasa da kasa na Portharcourt dake Omagwa.
- An tsare wani mataimakin ministan tsaron kasar Rasha bisa zargin karbar cin hanci
- An dakatar da Daraktan kwalejin Birnin Kudu da jami’in kula da harkokin abinchi na kwalejin
- Gwamna Namadi yayi kira ga sabbin masu yiwa kasa hidima da aka turo jihar jigawa da su kasance jakadu na gari
- Majalisar dokokin jihar Jigawa ta kafa kwamatin wucin gadi domin nazari kan dokar hukumar zabe
- Jam’iyyar PDP za ta gudanar da babban taronta a jihohi 25 domin zaben sabbin shugabanni
Sauran sun hadar da filin jirgin Sam Mbakwe na Owerri, da kuma na Maiduri, sai filin jirgin Victor Atta dake Uyo, da kuma na Kaduna da Yola.
Sirika ya kara da cewa a kwai tashar Ekpo na Calaba da kuma Sultan Abubakar dake Sokoto, sannan filayen jirgin sama na Birnin Kebbi da Yakubu Gowon da ke Jos, sannan tashar jirgin Benin dake Jihar Edo.
Ministan ya ce bayan kammala dukkan shirye-shirye, an amince da tashoshin jiragen guda 14 su dawo bakin aiki.