

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Shahararren Dan Fashin Dajin nan Bello Turji, ya bayyana dalilan da suka sanya ya zama daya daga cikin Rikakkun yan fashin Daji da suke addabar Arewacin Najeriya.
Bello Turji, ya yi kaurin suna wajen farmakar Arewacin Kasar nan fiye da shekaru, tare da kashe Dubban mutane, da kuma sace Dalilan Makarantu samu da 10 cikin shekara 1.
Manema Labarai sun rawaito cewa biyo bayan hare-haren Bello Turji, Dubban Kauyawa ne suka yi sansani a wuraren daban-daban, ya yinda wasu kuma suka samu mafaka a Jamhuriyar Nijar, biyo bayan gazawar gwamnati wajen basu kayan Jinkai.
Da yake zantawa da Manema Labarai, Bello Turji, ya ce ya shiga aikin fashin Daji ne biyo bayan yankan ragon da ake yiwa mutanan sa a Kasuwar Shinkafi.
Bello Turji, ya karyata labaran da ke cewa yana da Alkala da yan Kungiyar Boko Haram, inda ya ce basu da Alaka da Siyasa.
Kazalika, ya caccaki Matasan Yan Sakai, biyo bayan yadda suke hada hannu da Jami’an tsaro wajen Firgita Fulani.