

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sanya hannu akan kudirin dokar zabe da aka yiwa gyara kuma ya zama doka.
Shugaban Kasar ya sanya hannu akan kudirin a fadar shugaban kasa a gaban shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan, da kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila, da sauran jami’an gwamnati.
Sanya hannu akan kudirin yazo ne kwanaki kadan bayan kakakin shugaban kasa, Femi Adesina, ya tabbatar da cewa shugaba Buhari zai sanya hannu akan kudirin.
Kafin ya sanya hannu akan kudirin, shugaban kasar ya nemi a yiwa kudirin gyara inda ya bukaci majalisun kasa su goge wani sashe na kudirin wanda ya haramtawa masu rike da mukaman siyasa tsayawa takara a zabe.
Shugaban kasar yace sashen ya dakile yancin masu rike da mukaman siyasa na tsayawa takara a zabe da zaben wani dan takara a dukkanin tarukan jam’iyyun siyasar kasarnan.