

Dakarun ƙungiyar Islamic State of West Africa Province (ISWAP) da iyalansu 104 sun miƙa wuya ga sojojin Najeriya, a cewar rundunar sojan ƙasar.
Wata sanarwa da ta wallafa a shafukanta na zumunta, rundunar ta ce mayaƙan da suka yi saranda a ranar Asabar sun ƙunshi maza 22 da mata 27 da yara 55.
Ta ƙara da cewa sun kai kan su ne ga dakarun rundunar musamman ta 25 da ke Damboa a Jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.
Yaƙin Boko Haram ya yi sanadiyyar kisan mutum aƙalla 300,000 sannan ya raba fiye da miliyan 2.5 da muhallansu, a cewar alƙaluman Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD).