

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Majalisar Wakilai ta Kasa ta sanar da shirinta na komawa bakin aiki da zaman majalisar, a ranar gobe Talata.
Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da magatakardan majalisar, Patrick Giwa, ya aikewa dukkan ‘yan majalisar.
Majalisar a watan Maris da ya gabata ta dage zamanta na tsawon makonni 2, a kokarin dakile bazuwar cutar corona. Daga baya ta kara wa’adin dagewar domin ta dace da dokar kulle a babban birnin tarayya.
Dangane da matakan kariya, Mista Giwa yace za a aikawa ‘yan majalisar sharuddan kare kai daga cutar corona da gwamnatin tarayya da cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC suka amince da su, da karin wasu sharuddan da majalisar ta samar.
Sai dai yace ma’aikata da hadiman ‘yan majalisar zasu cigaba da aiki daga gida, kuma za a sanar da su dukkan lokacin da ake bukatarsu a wajen aiki domin wani aiki na musamman.