Damagum Ya Mika Ragamar Shugabancin Jam’iyyar PDP Zuwa Sabon Kwamatin NWC Karkashin Jagorancin Tanimu Turaki

0 312

Tsohon mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP, Umar Damagum, ya mika ragamar mulki ga sabon kwamitin gudanarwar jam’iyyar (NWC) karkashin jagorancin Tanimu Turaki.

Wa’adin kwamitin Damagum zai kare ne a ranar 8 ga Disamba, 2025, bayan wani rikicin shugabanci tsakaninsa da bangaren da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ke mara wa baya.

An gudanar da bikin mika mulkin ne a Gidan Gwamnan Bauchi da ke Abuja.

Da yake jawabi, Damagum ya ce sabon NWC ya samu cikakkiyar dama da daukar nauyin farfado da hadin kan PDP. Ya ce:

“Abin alfahari shi ne mun sha wahalhalu sosai, amma mun tsallake su, kuma za mu ci gaba da tsallake kowace barazana”.

Damagum ya kara da cewa makomar PDP akwai haske a gaba, sannan har yanzu ita ce jam’iyyar da ake tsoro a fafutukar siyasa a Najeriya.

“Shi ya sa suke kasa barci saboda PDP. Suna ta kakabawa jam’iyya kalubale iri-iri, amma Allah zai tabbatar mana da nasara. Mun tabbata, Allah mai adalci ne kuma baya goyon bayan zalunci”.

Ya kuma yi gargadi cewa wadanda ke tayar da rikici a jam’iyyar suna iya fuskantar hukunci, hukuncin aikinsu zai zo nan gaba.

A nasa jawabin, sabon shugaban NWC, Tanimu Turaki, ya yabawa kwamitin kan kokarin da suka yi. Ya kuma yi alkawarin cewa zai ci gaba da aiki tukuru don inganta cigaban PDP.

Leave a Reply