

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Darakta-Janar na Hukumar Bunkasa Fasahar Sadarwa ta Kasa (NITDA), Kashifu Inuwa, ya bayar da tabbacin hukumar na hadin gwiwa da Cibiyar Horas da Ma’aikata ta Jihar Jigawa (Manpower) domin bayar da horo kan ilimin na’ura mai kwakwalwa a jiharnan.
Darakta Janar din ya ce hakan ya yi daidai da aikin NITDA na inganta cigaban rayuwar dan Adam ta hanyar aiwatar da tsare-tsarenta.
Kashifu Inuwa ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin Shugaban Hukumar Gudanarwa na Cibiyar ta Manpower, Inuwa Tahir, da tawagarsa a wata ziyarar ban girma da suka kai a hedikwatar NITDA da ke Abuja.
Darakta Janar din ya ce matakin na hadin gwiwa tsakanin hukumomin biyu ya zo a kan lokaci, ganin yadda bunkasa ma’aikata da inganta ayyukan su ne manyan abubuwan da shugaban kasa Muhammad Buhari ya sanya a gaba, wanda ya sa aka kafa wani kwamiti kan yadda kasarnan za ta fita daga cikin koma bayan tattalin arziki.