Duk wanda aka kama zai yaba wa aya zaki, gwamnatin Kaduna ba ta nada kwamitin yin sulhu da ‘Yan bindiga ba

0 88

Gwamnatin jihar Kaduna ta gargadi masu yayada cewa wai ta nada kwamitin yin sulhu da’ Yan bindiga a madadin gwamnatin a jihar da su shiga taitayin su tunda wuri ko kuma su yaba wa aya zaki.

A wata takarda da kwamishinan tsaron jihar, Samuel Aruwan ya fitar ranar Lahadi, gwamnatin jihar ta karyata wannan labari da ya karade shafukan jaridu da na sada zumunta a yanar gizo.

” An jawo hankalin gwamnatin Kaduna karkashin jagorancin gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, wai gwamnati ta nada kwamiti domin yin sulhu da ‘yan bindiga a jihar.

” Muna so mu tattabar wa mutane cewa wannan magana babu gaskiya a cikin sa, sannan kuma tuni har gwamnati ta dana tarkon kama duk wanda sune suka kirkiro wannan abu da kuma wadanda ke da hannu wajen kirkiro kwamitin karyar.

” Matsayar gwamnatin Kaduna kan ‘ Yan bindiga na nan daram, ba za ta yi sulhu da su ba. Duk wanda yake yin haka a madadin gwamnatin jihar, ya sani ba da dawun gwamnati yake yi ba, idan kuma aka kamashi ko shi waye, Kotu za ta raba su da gwamnati.

Idan ba a manta ba gwamnan jihar Kaduna El-Rufai, ya fadi ya kuma kara jaddadawa cewa gwamnatin sa ba za ta biya mudin fansar wani ga mahara. El-Rufai ya ce yin sulhu da mahara ba shi bane abin yi kuma gwamnatin sa ba za ta yi haka ba.

A ra’ayin gwanma El-Rufai, a bisu inda suke a ragargaje su shine kawai mafita, amma a rika bi ana dankara musu kudi na babu gaira babu dalili, zai basu karfin guiwar ci gaba da abinda suke yi ne.

Leave a Reply

%d bloggers like this: