ECOWAS ta himmatu wajen magance matsalolin tsaro – Tinubu

0 165

Shugaban kasa Bola Tinubu yace kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS ta himmatu matuka gaya wajen tabbatar da kyakkyawan shugabanci da magance matsalolin tsaro.

Ya bayyana hakan ne a Birnin Beijing na kasar China, lokacin da yake jawabi a wani taron shugabanni kan zaman lafiya da tsaro na bana da hadin kai tsakanin kasashen Afrika da China.

Tinubu yace a Najeriya gwamnatin sa ta mayar da hankali wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a tsakanin kashen yammacin Afrika.

Ya kuma yabawa tallafin kasar China wajen bunkasa cigaban nahiyar Afrika.

Tinubu ya kuma bayyana muhimmancin aukawar matsalolin tsaro tun daga tushe, kamar talauci, rashin dai-daito, da rashin adalcin zamantakewa, yana mai cewa matukar za’a kawo sauyi, ya zama wajibi, a samar da adalci, daidaito, samar da damarmakin tatalin arziki da bunkasa tsaron dan adam.

Leave a Reply