Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, ya bukaci gwamnoni da su kara zuba jari a bangaren gona

0 98

Gwamnan Babban Bankin Kasa (CBN), Godwin Emefiele, ya bukaci gwamnoni jihoshi 36 da su kara zuba jari a bangaren gona domin habaka tattalin arzikin jihoshinsu.

Emefiele wanda yayi jawabi a Fatakwal a jiya a wajen kaddamar da kamfanin sarrafa rogo na jihar Rivers, yace gwamnoni su zuba jari a amfanin gonar da suke da shi.

Gwamnan na CBN yace kamfanin zai taimaka wajen inganta samarwa da sarrafa rogo zuwa garin fulawa mai inganci a jihar Rivers.

Emefiele yayi nuni da cewa samar da gonaki ne babbar matsalar da ake fuskantar wajen ayyukan noma a yankunan kudancin kasarnan saboda yanayin kasar can.

Ya kuma ce jihoshin yankin kudu maso kudu sun ci gajiyar kimanin naira biliyan 7 da miliyan 436 domin samar da karin gonakin noma, da samar da hanyoyin zuwa gonaki, da samar da kayan aikin gona, da sauran abubuwan tallafi a yankin.

Leave a Reply

%d bloggers like this: