Gwamnatin Masar tayi tayin taimakawa Najeriya wajen adana tagulla fiye da dubu daya

0 76

Gwamnatin Masar ta yi kan tayin taimakawa Najeriya wajen adana tagulla 1,130 na kasar Benin da ake sa ran a kasar daga Jamus.

Kayayyakin tarihi masu nauyin kilogiram 30 kowanne, wadanda sojojin Birtaniya suka wawashe a shekarar 1897, za a dawo da su daga Jamus zuwa Najeriya a wannan shekara.

Ministan yawon bude ido da kayayyakin tarihi na kasar Masar, Khaled El-Anany, ya yi wannan tayin a birnin Alkahira na kasar Masar lokacin da ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed, ya kai masa ziyara.

Taron dai ya zo ne a daidai lokacin da ake tattaunawa da bankin Africa Export-Import Bank kan yadda Najeriya za ta iya samun kudade don tallafawa masana’antar kere-kere da ke bunkasa.

Mohammed ya jagoranci wasu masu ruwa da tsaki na kamfanoni masu zaman kansu da ke da hannu a cikin Digital Switch don taimaka musu kan yadda za su iya samun kudade don kammala ayyukan kamfanoni masu zaman kansu gaba ɗaya.

Ministan Masar din ya ce a shirye suke su yi amfani da dukiyoyinsu na gogewa wajen kula da adana kayan tarihi don taimakawa Najeriya wajen adana dukiyar da ake sa ran daga Jamus.

Leave a Reply

%d bloggers like this: