Gwamnatin Najeriya Ta Musanta Batun Karin Haraji Kan Sadarwa da Mai

0 84

Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata rahotannin da ke cewa tana shirin ƙara sabbin haraji kan harkokin sadarwa ta waya da kuma man fetur, tana mai cewa waɗannan rahotanni ba su nuna gaskiyar manufofinta ba.

Wannan bayanin ya biyo bayan wasu rahotanni da suka danganta da shawarwarin Asusun Lamuni na Duniya (IMF), wanda ya ce Najeriya na iya ƙara harajin VAT kan man fetur da hukumomin sadarwa ta waya domin ƙara kudaden shiga da tallafa wa ci gaba.

Sai dai a wata sanarwa da ma’aikatar kudi ta fitar, ta bayyana cewa shawarar IMF ba dole ba ce, kuma ba ta zama doka ga Najeriya ba, domin duk wani mataki na haraji sai an bi tsarin doka da majalisa tare da la’akari da halin tattalin arzikin ƙasa.

Gwamnatin ta ƙara da cewa har yanzu ana ci gaba da dakatar da harajin VAT kan man fetur, haka kuma an soke harajin sadarwar waya da aka gabatar kafin shekarar 2023, tana mai jaddada cewa babu wani sabon haraji da ake shirin ƙaƙabawa a yanzu.

Leave a Reply