Gwamnatin Tarayya ta samu nasarar dakile tafiya yajin aiki sama da sau dubu 4

0 128

Gwamnatin Tarayya tace ta samu nasarar dakile tafiya yajin aiki sama da sau dubu 4 daga kungiyoyin ma’aikata a fadin kasarnan ta hanyar tattaunawar sulhu cikin shekaru 7 da suka gabata.

Ministan kwadago da aikin yi, Dr Chris Ngige, shine ya sanar da haka a wajen taron manema labarai na ministoci da ake yi sau biu kowane sati wanda tawagar sadarwar shugaban kasa ta shirya jiya a Abuja.

A cewarsa, tattaunawar sulhu ita ce hanya mafi kyau wajen sassanta rikicin kwadago.

Chris Ngige ya kara da cewa ma’aikatar na da teburan sassan rikicin kwadago da bayar da daukin gaggawa a dukkanin jihohin kasarnan wadanda suka taimaka wajen magance rikice-rikicen ma’aikata.

A cewar ministan, tuni aka fara tsare-tsaren karin albashi ga ma’aikata musamman wadanda ke karbar alawus-alawus na musamman, inda ya kara da cewa hukumomi na jiran amincewar shugaban kasa ne kadai domin fara aiwatarwa. Ministan ya kara sanar da cewa Najeriya ta kammala shirye-shiryen hada kai da hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya domin hana ‘yan kasarnan tafiya neman aiki kasashen waje ba bisa ka’ida ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: