

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Kungiyar Gwamnonin Arewa tana bukatar kudade na musamman daga gwamnatin tarayya domin dakile yaduwar COVID-19 a yankin Arewa.
Shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Filato, Simon Lalong, shine yayi kiran a wata sanarwa da daraktan yada labaransa, Dr. Makut Machan ya fitar a Jos, bayan ganawar gwamnonin kungiyar ta hanyar faifan bidiyo.

A cewar sanarwar, shugaban yayi zargin cewa an bawa sauran jihoshi wasu kudade na musamman, amma babu wata jiha a Arewa da aka bata, duk da kasancewar an samu bullar cutar a Arewa.
Simon Lalong yace yankin na Arewa yana kokarin fadada hanyoyin tattalin arzikinsa a bangarorin da yake da karfi, domin rage dogaro kacokan da gwamnatin tarayya.