

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Hukumar Hisbah a Jihar Kano ta tabbatar da kama gungun wasu matasa maza da mata su 78 suna tsaka da aikata masha’a a wani gidan casu mai suna ‘White House’ a unguwar Nassarawa GRA.
Shugaban Hukumar, Harun Ibn Sina, ya shaida wa manema cewa sun kama matasan ne bisa zargin aikata fasadi da kuma yin shiga ta bayyana tsiraici, amma ya karyata rade-radin da ke yawo cewan an kama matasan ne suna hada auren jinsi a tsakaninsu.
Wadanda ake zargin sun kunshi da maza da mata.
Ya kara da cewa matasan sun musanta cewa auren jinsi suke daurawa, shagalin bikin zagayowar ranar haihuwar dayansu suke yi.
Shugaban hukumar ya ce wadanda aka kama din suna tsare a hannun hukumar.