

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Hukumar cigaban fasahar sadarwa ta kasa (NITDA) ta fara bayar da horo ga alkalan kotunan daukaka kara akan ilimin komfuta.
Ministan sadarwa da tattalin arziki na zamani, Isa Ali Ibrahim Pantami, wanda ya samu wakilcin Darakta Janar na NITDA, Kashifu Inuwa Abdullahi, shine ya bayyana aikin bayar da horon a matsayin wanda ake yi a lokacin da ya dace, inda yace bangaren shari’ah na da muhimmiyar rawar da zai taka a shirin mayar da ayyukan gwamnati zuwa na komfuta.
Wata sanarwa daga hukumar NITDA ta rawaito ministan na cewa karuwar barazanar da ake samu daga guraren da babu jami’an tsaro ya sanya hukumar NITDA ta hada kai da kotun daukaka kara wajen bayar da horo ga alkalan da nufin kare demokradiyya da tsaron kasarnan.
Isa Pantami ya kara da cewa abune da ya dace ga bangaren shari’ah a matsayin manyan abokan hulda ga cigaban tattalin arzikin kasarnan su rungumi fasahar sadarwa hannu bibiyu, da nufin bunkasa ayyukansu domin samun cigaba.