- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Hukumar Bunkasa Fasahar Sadarwa ta Kasa, NITDA, ta fara kaddamar da wani shirin horas da matasa 50 masu yi wa kasa hidima (NYSC) akan aikin gona.
An fara horon ne a yau a Abuja tare da hadin gwiwar cibiyar fasahar kere-kere dake karkashin hukumar, da kuma cibiyar fasaha ta Abuja.
Horon dai wani bangare ne na ayyukan hukumar na tabbatar da cewa dukkan bangarorin kasar nan suna tafiyar da ayyukansu ta hanyar fasahar sadarwa.
Babban Daraktan NITDA, Kashifu Inuwa, ya bukaci mahalarta taron da su yi amfani da wannan dama tare da nuna sha’awar kasuwancin noma bil hakki.
Kashifu Inuwa wanda ya samu wakilcin Salisu Kaka, Daraktan riko na sashin bunkasa tattalin arzikin zamani na NITDA, ya ce dabarun da za a koya za su baiwa mahalarta taron damar samar da ayyukan yi.