Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Kwamitin ayyuka na jam’iyyar PDP na kasa ya tsawaita ranakun siyar da form din tsayawa takara da nuna sha’awar takara a zaben 2023 da mako guda.
Jam’iyyar PDP ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa jiya ta hannun sakataren yada labaranta na kasa, Debo Ologunagba, da ya fitar a Abuja.
Debo Ologunagba ya ce an kara wa’adin ne daga gobe Juma’a 1 ga watan Afrilu zuwa 8 ga Afrilun gobe.
Sakataren Yada Labarai na Kasa ya ce jam’iyyar ta kuma dage ranar tantance masu neman kujerar majalisar wakilai zuwa ranar 12 ga watan Afrilu yayin da za a gudanar da tantance masu neman takarar majalisun tarayya a ranar 14 ga Afrilu.