

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Hukumar bunkasa fasahar sadarwa ta kasa (NITDA) ta fara shirin horas da masu sana’o’in hannu da matasa akan ilimin komfuta da gyaran wayoyin hannu.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar a Abuja ta hannun shugabar sashen yada labarai na hukumar, Hadiza Umar, kuma aka bawa kamfanin dillancin labarai na kasa.
Sanarwar tace aikin horon, wanda aka fara a jiya, zai habaka ilimin komfuta da samar da sana’o’i ga matasan Najeriya tare da ilimomin da ake bukata wajen samar da sana’o’i.
Sanarwar ta kuma ce an shirya bayar da horon ne da nufin dakile tulin matsalolin dake fuskantar kasarnan musamman karancin ilimin sana’o’i tsakankanin dumbin matasan da basu da aikin yi.
Sanarwar ta kara da cewa za a gudanar da aikin bayar da horon a jihoshi 4 na Gombe, Kogi, Neja da Oyo.