Jama’a su rika kare da kuma kula da ayyukan gwamnati a yankunansu – Akpabio

0 364

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bukaci al’ummar Najeriya da su rika kare da kula da ayyukan raya ƙasa da gwamnati ke aiwatarwa a yankunansu.

Akpabio, wanda ya bayyana haka yayin kaddamar da wasu ayyuka a karamar hukumar Ika ta jihar Akwa Ibom, ya ce kamata ya yi al’umma su ɗauki wadannan ayyuka a matsayin na su domin gujewa lalacewa.

Ya ƙara da cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na ƙoƙarin rage raɗaɗin rayuwa ta hanyar samar da tallafi da kuma ingantattun ayyuka ga talakawa.

Leave a Reply