Rahotanni daga iyalin tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sun ce jami’an tsaro sun sake kama shi jim kaɗan bayan fitowarsa daga kotu a yau, Talata.
Wata majiya daga cikin iyalinsa ta shaida wa BBC cewa an kama shi ne a wajen harabar kotun, lamarin da ya jefa iyalansa da magoya bayansa cikin damuwa.
Majiyar ta kuma ce bayan kammala sauraron buƙatar ba da belinsa ne aka yi awon gaba da shi, inda suka sa ran Abuja za a kai shi.
Har yanzu ba a bayyana cikakken dalilin sake kamen nasa ba, amma ana zargin yana da alaƙa da binciken da hukumomi ke ci gaba da yi a kansa.
Sai dai har yanzu hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance da ke bayani kan lamarin ba.