

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Jamiar Tarayya dake Dutse tace ta sayi Kimanin littafai 500 da mujallu 1000 wanda kudinsu ya kai naira miliyan 100 da nufin bunkasa karatun dalibai a jami’ar, bugu da kari jamiar ta kuma kammala duk wasu shirye-shirye domin karba da gudanar da asibitin Rasheed Shokini wanda zai kasance asibitin koyarwa na jami’ar.
Mataimakin Shugaban jami’ar Farfesa Abdulkadir Muhammad Sabo ne ya bayyana yayin taron manema labaran daya kira a jiya don bayyana irin nasarorin daya cimma bayan karbar ragamar jagorancin jami’ar tsawon shekara guda. Yace jami’ar ta sami nasarar biyan dukkanin bassusukan da ma’aikatan jamiar ke bin ta.
Wakilinmu na Dutse Zulkiflu Abdallah Dagu ya kasance a wajen taron manema labaran ga kuma rahotan daya hada mana.