Karamar Hukumar Kazaure ta biya miliyan 2.4 domin tallafawa daliban yankin dake karatu a jami’ar SLU

0 191

Karamar Hukumar Kazaure ta ce ta kashe kudi naira miliyan biyu da dubu dari hudu da arbain wajen biyan tallafin karatu ga daliban yankin dake karatu a Jami-ar Sule Lamido Kafin Hausa

Shugaban KH Alhaji Mansur Usman Dabuwa ya sanar da hakan a lokacin rabon tallafin karatun a harabar Jamiar

Ya kara da cewar kusan dalibai 204 ne suka ci gajiyar shirin a wani mataki na bunkasa harkokin karatu

Alhaji Mansur Usman Dabuwa ya kuma ce KH ta kashe kudi naira miliyan daya da rabi wajen samar da littattafan rubutu da alli da sauran kayayyakin koyo da koyarwa a makarantun firamare da kuma kananan makarantun sikandaren yankin

A jawabinsa Darakta maaikata na yankin Alhaji Shu’aibu Naa’abo  ya bukaci daliban da su maida hankali wajen yin karatu

Shima da yake jawabi sakataren harkokin malamai na  jamiar Malam Izaddin Ibrahim Dan Malikin Taura ya yabawa shugaban KH bisa wannan karamci wanda hakan zai karawa dalibai kwarin gwiwa wajen yin karatu

Shima shugaban kungiyar dalibai na jamiar Sule Lamido Comrade Adamu Musa ya yaba da kokarin gwamnatin jiha na bunkasa harkokin ilmi

Leave a Reply