

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Kwanaki biyu bayan da ‘yan bindiga suka kashe ‘yan sa kai 63, ‘yan bindigar sun sake kashe jami’an tsaro 19 a cikin tawagar mataimakin gwamnan jihar Kebbi, Samaila Yombe, a kauyen Kanya da ke karamar hukumar Danko Wasagu ta jihar.
Lamarin na baya-bayan nan ya faru ne a ziyarar da mataimakin gwamnan ya kai yankunan jihar da hare-haren ‘yan bindigar ya shafa.
Majiyoyi da dama sun ce ‘yan bindigar sun auka wa mataimakin gwamnan, Samaila Yombe, wanda dan asalin garin Dabai ne a karamar hukumar Zuru.
Mataimakin gwamnan ya tabbatarwa da BBC Hausa a yammacin jiya cewa yana kauyen lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari.
Wani dan karamar hukumar Danko Wasagu, Labaran Magaji, ya shaidawa manema labarai cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen Kanya da misalin karfe 5 na yamma.
A cewar Labaran Magaji, an kashe sojoji 13 da jami’an ‘yan sanda shida da ke tare da ayarin mataimakin gwamnan.