- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Ma’aikatar harkokin Kasashen waje ta sanar da cewa, a gobe ne ake sa ran za ta karbi kashin farko na ‘yan Najeriya da aka kwaso daga kasar Ukraine.
Babban sakataren ma’aikatar, Gabriel Aduda ne ya sanar da hakan.
A cewar Gabriel Aduda, jiragen da aka yi hayar su, Air Peace da Max Air, za su tashi a yau domin dauko ‘yan Najeriya da za kwaso zuwa gida.
Ya kara da cewa, ofisoshin jakadancin Najeriya a kasashen Hungary, Poland, Romania da Slovakia sun karbi ‘yan Najeriya daga kasar Ukraine.
Gabriel Aduda ya sanar da cewa Max Air zai kwaso Dalibai 560 daga Romania yayin da Air Peace zai kwaso mutane 364 daga Poland da 360 daga Hungary.
A ranar Litinin ne gwamnatin tarayya ta bayyana cewa daga yau za ta fara kwaso ‘yan Najeriya daga kasar Ukraine.