Majalisar Wakilai ta bayyana dalilan da suka sa ta wanke Alhaji Mohammed Bello Koko

0 123

Majalisar Wakilai ta bayyana dalilan da suka sa ta wanke Shugaban Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya NPA, Alhaji Mohammed Bello Koko daga zarge-zargen badaqalar bashin naira biliyan 178 da ke tattare a rahoton yadda hukumar ta gudanar da ayyukanta na shekarar 2019.

Shugaban kwamitin majalisar wakilai da ke sauraron korafe-korafe, Hon Mike Etaba, ya bayyana mastayar majalisar a zaman bayyanar jama’a da aka yi aAbuja a makon da ya gabata.

Idan za a iya tunawa wata kungiya mai zaman kanta ta zargi hukumar da Bello-Koko a kan badakalar naira biliyan 178 na kudaden da suka makale daga basukan da hukumar take bi wadanda ke tatteare a cikin rahotonin hukumar na shekarar 2019.

A yayin da aka ci gaba da zaman sauraron matsalar na bayyanar jama’a, kungiyar ba ta bayyana ba don ta kare zarge-zargen da ta ke yi a kan haka kwamitin ya yi watsi da zarge-zargen gaba daya. Shugaban kwamitin Hon. Eytaba ya nuna takaicinsa a kan rashin bayyanar wadanda suka yi zargin don su kare tare da gabatar da hujjojin da ya kamata a kan haka ya yi watsi da zargin da suke yi wa NPA da shugabanta, Alhaji Mohammed Bello Kpko.

Leave a Reply

%d bloggers like this: