

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Masu fafutukar kare mulkin demokradiyya a kasar Sudan sun sanar da sabbin zanga-zanga daidai lokacin da rikicin siyasa ya kara muni bayan murabus din Fira-Ministan Abdalla Hamdok a jiya.
Akalla masu zanga-zanga 3 aka kashe a ranar Lahadi bayan dubban masu zanga-zangar dake adawa da mulkin sojoji suka bazama kan tituna.
Adadin masu zanga-zangar da aka kashe tun bayan juyin mulkin sojoji na watan Oktoba ya karu zuwa 56.
Kungiyar kwararrun kasar Sudan, gamayyar kungiyoyin ma’aikata, dake jagorantar zanga-zangar adawa da mulkin sojoji, tace masu zanga-zangar zasu tunkari fadar shugaban kasa.
Shugaban kasar na mulkin soja, Laftanar Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya gayawa jagororin soja a jiya cewa sojojine jigon tsaron kasar kuma zasu kare tsarin mika mulki ga fararen hula.
Jakadan majalisar dinkin duniya a Sudan, Volker Perthes, yace yayi takaicin matakin Abdallah Hamdok na yin murabus.