Ministan tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya gabatar da shirinsa kan makomar Gaza

0 193

Ministan tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya gabatar da shirinsa kan makomar Gaza, bayan kammala yaƙi.

Amurka ta daɗe tana matsa wa gwamnatin Isra’ila lamba da ta bayyana shirinta a fili.

Yoav Galanta ya ce Falasdinawa ne ke rayuwa a Gaza, don haka za su ci gaba da jagorancin yankin, amma bisa sharaɗin cewa babu zaman doya da manja da Isra’ila, kuma babu shirya mata wata kutungwila. A cewarsa, yanzu yaƙin da Isra’ila ke yi a zirin zai fi mayar da hankali kan kudancin yankin, kana za su ci gaba da ƙoƙarin ganin sun kashe shugabannin ƙungiyar Hamas, ko a ina suke a doron duniya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: