Ministan wutar lantarki ya sha alwashin gwamnatin tarayya zata inganta wutar lantarki
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2021/08/NEPA-3.jpg?resize=612%2C408&ssl=1)
Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya sha alwashin cewa gwamnatin tarayya za ta samar da wutar lantarki ga al’ummomin da ba su amfani da wutar lantarkin a Najeriya.
Ministan ya bayyana haka ne a jiya Litinin yayin da yake duba aikin tare da tantance tasirin wutar mai karfin kilo watt 90 a Adafila, Ogbomoso, a wani bangare na rangadin aikin da ya ke yi na samar da wutar lantarki a Najeriya.
Adelabu ya ce aikin zai iya samarda wutar lantarki ga gidaje sama da 1,300 da suka hada da dakunan shan magani, makarantu, da kananan ‘yan kasuwa a cikin al’umma. Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa tun da farko ministan ya kai ziyarar dudduba ayukka a tashoshin samar da wutar lantarki mai karfin kilo vat 132 a Oyo da Ogbomoso.