

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Jakadiyar Najeriya a Romania da ke makwabtaka da Ukraine ta ce zuwa yanzu sun karɓi ƴan ƙasar kusan 200 yawancinsu ɗalibai da suka tsallako Bucharest babban birnin ƙasar daga Ukraine.
Safiya Nuhu ta shaida wa BBC cewa suna kyautata zaton samun adadin ƴan Najeriyar fiye da haka da ke tserewa daga Ukraine.
“Mun tarbe su kuma mun ba su masauki a otel otel a Bucharest,” in ji ta.
Ɗaruruwan ƴan Najeriya ne suka tsallaka kan iyakar Ukraine, inda ake sa ran kwashe su zuwa birane mafiya aminci, kafin mayar da su Najeriya.
Sai dai yawancinsu da sauran ƴan Afirka sun yi ƙorafi kan yadda ake nuna masu wariya a kan iyakar Ukraine da Poland.
BBCHausa